Kusan mutum 200 aka kashe a Katsina da Borno a makon da ya gabata
Mun tsakuro muku muhimmai daga cikinsu.
'Yan Boko Haram sun kashe mutum 90 a Borno, 'Yan bindiga sun hallaka sama da 100 a Katsina

A makon da ya gabata ne aka samu rahotanni daga jihohi biyu na arewacin Najeriya kan cewa an kashe farar hula kusan 200 a hare-haren da aka ƙaddamar kan al'ummomi a jihohin Borno da Katsina.
A yankin arewa maso yammacin ƙasar, mazauna yankin sun shaida wa BBC cewa an kashe mutum fiye da 50 a hare-haren 'yan bindiga a ƙauyen Ƙadisau da ke ƙaramar hukumar Faskari ta jihar Katsina, sa'annan daga baya aka kai hari a garuruwan 'Yan kara da Faskari da 'Yan Tumaki da Dan Ali inda aka kashe sama da mutum 50.
Bayanan nan kuma 'yan bindigan sun je garin Mazoji a jihar ta Katsina inda suka kashe Mai Garin.
0 Comments: