Sunday, June 14, 2020

Rasha da Turkiyya za su tattauna kan rikicin Libya





Ana sa rai ministocin wajen Turkiyya da na Rasha za su tattauna kan ƙoƙarin kawo ƙarshen yaƙin da ake gwabzawa a Libya, yayin wata ganawa da za su yi ranar Lahadin nan a birnin Istanbul.

Gwamnatin birnin Ankara da takwararta ta Moscow na goyon bayan ɓangarori daban-daban na rikicin, wanda ya yi sanadin raba dubun dabatar mutane daga gidajensu tun daga watan Afrilun bara.

Turkiyya na mara baya wa gwamnati mai sansani a Tripoli, babban birnin ƙasar, yayin da Rasha ke goyon bayan Janar Khalifa Haftar, wanda ya fuskanci ɓacin rana cikin ƴan makwannin nan a hannun dakarun gwamnati.

Duka Turkiyya da Rasha a baya-bayan nan sun ce suna son ɓullo da wnai yanayi na tattaunawa da sasanta tsakani.

Previous Post
Next Post

0 Comments: