Sunday, June 14, 2020

Mutane na gudun hijira a yankunan Katsina

Mutane na gudun hijira a yankunan Katsina

Al'ummomin ƙauyukan yankin Katsina musamman mata da yara na ci gaba da tserewa daga gidajensu saboda ƴan fashin daji da suka addabe su da hare-hare.

Wani mazaunin yankin Hassan Mohammed Daudawa ya shaida wa BBC cewa mutanen sun koma rayuwa a cikin azuzuwan wasu makarantun Boko na yankin Funtua da sauran yankunan da ba a cika kai hare-hare ba.

A ƴan kwanakin nan ƴan bindiga masu fashin daji sun tsawwala hare-hare a yankunan karkara na Katsina inda ko a ranar Juma'a sun shiga garin Mazoji na karamar hukumar Matazu suka kashe Mai Garin Papu Alhaji Dikko Usman Mazoji bayan sun kashe Hakimin Ƴantumaki a makon da ya gabata wanda ya haifar da zanga-zanga a garin.

Maharan sun kuma sun kuma shiga garin Ƴankara da sauran kauyuka a karamar hukumar Faskari da kuma wasu ƙauyuka na Batsari inda suka kashe mutane suka kuma tafi da wasu da dabbobi.

Ga Hirar Abdou Halilou da Hassan Mohammed Daudawa

Video content

Video caption: Mutane na gudun hijira a yankunan Katsina
Previous Post
Next Post

0 Comments: