Tuesday, May 31, 2022

Ina sa ran daliget za su zabe ni ko ban ba su kudi ba – Badaru

Ina sa ran daliget za su zabe ni ko ban ba su kudi ba – Badaru

 

Bayanan bidiyo,

Delegate za su zabe ni ko ban ba su kudi ba - Gwamna Badaru

Daya daga masu neman jam'iyyar APC ta tsayar da su takarar shugaban kasa Muhammad Badaru Abubakar ya ce wakilan da za su fitar da dan takara za su zabe shi saboda suna ganin mutuncinsa.

Badaru Abubakar wanda ya kasance gwamnan jihar Jigawa, ya kuma ce amincewar da ya tabbata yaa da ita a wajen 'yan deliget-deliget ne ya sanya ya furta wadannan kalaman.

Cikin wannan hirar da yayi da BBC, Gwamna Badaru ya bayyana wasu dalilai da a ganinsa za su ba masu zaben dan takara karfin gwuiwar zabensa.

Cikin abubuwan da ya bayyana akwai gogewar da ya samu bayan ya shafe shekaru yana aikin gwamnati da kuma kasuwanci.

Danna hoton Gwamnan da ke sama domin sauraren yadda hirar ta kasance da Zaharadeen Lawan.

APC na tantance Osinbajo, Lawan, Bello da sauran masu neman takarar shugaban Najeriya


 

 

 

A ranar Talata ne ake sa ran kwamitin da ke tantance masu neman tsayawa takarar shugaban ƙasar Najeriya ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban Jam'iyyar APC, John Oyegun, zai ci gaba da tantance sauran masu neman tsayawa takara.

Ranar Litinin ne kwamitin ya soma tantance masu neman takarar.

Ana tantance masu neman takarar ne gabannin gudanar da zaɓen fitar da gwanin da za a gudanar na jam'iyyar tsakanin shida zuwa takwas ga watan Yunin 2022.

Ana gudanar da aikin tantancewar ne a otal ɗin Transcorp Hilton da ke Abuja babban birnin Najeriya.

Cikin waɗanda aka tantance a karon farko akwai tsohon gwamnan Jihar Legas Bola Tinubu da Gwamnan Jigawa Abubakar Badaru da tsohon Ministan Sufuri Chibuike Amaechi da tsohon Gwamnan Ogun Ibikunle Amosun.

Sauran sun haɗa da tsohon ƙaramin Ministan Ilimi Chukwuemeka Nwajiuba da Gwamnan Ebonyi Dave Umahi da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa Ken Nnamani da tsohon Gwamnan Zamfara Sani Yarima.

Akwai kuma Felix Nicholas da Sanata Borroffice da Mrs Uju Ken-Ohaneye da Fasto Tunde Bakare

Sauran masu neman takarar da za a tantance a ranar Talata 31 ga watan Mayu kuwa sun haɗa da:

Yemi Osinbajo

 
 
Asalin hoton, YEMI OSINBAJO

 Mataimakin shugaban Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo na daya daga cikin na farko-farko da suka bayyana aniyarsu ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2023.Osinbajo, wanda daga Kwamishinan Shari'a na Jihar Legas ya zama mataimakin shugaban ƙasa na ɗaya daga cikin waɗanda ake sa ran za a tantance a ranar Talata.

Kayode Fayemi

 

 

 

 

Asalin hoton, Twitter

Gwamnan Jihar Ekiti kuma shugaban gwamnonin Najeriya Kayode Fayemi na daga cikin waɗanda ake sa ran za a tantance su a ranar Talata.

Gwamna Fayemi ya kasance ministan albarkatun ƙasa a lokacin mulkin Shugaba Buhari daga 2015 zuwa 2018 kafin ya tsaya takarar gwamna karo na biyu wanda dama ya taba yin gwamnan Jihar Ekiti daga 2010 zuwa 2014.

Ahmed Lawan

 

 

 

 

 

Asalin hoton, Twitter/@sen_ahmedlawal

Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Ahmed Lawan na daga cikin waɗanda za a tantance domin tsayawa takar shugaban ƙasa ƙarƙashin Jam'iyyar APC a ranar Talata.

Sanata Lawan wanda asalin ɗan Jihar Yobe ne, ya soma wakilci tun daga 1999 a matsayin ɗan Majalisar Wakilai, inda a 2007 ya koma Majalisar Dattawa kuma har yanzu yana a majalisa.

Yahaya Bello

Asalin hoton, YAHAYA BELO/FACEBOOK


 

Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello na daga cikin waɗanda ke neman tsayawa takarar shugabancin Najeriya a ƙarƙashin Jam'iyyar APC.

Yahaya Bello kusan shi ne ke da mafi karancin shekaru cikin mutanen da suka fito karkashin inuwar jam'iyyar APC suna neman mulkin Najeriya. Gwamnan yana da shekaru 46 a duniya.

Rochas Okorocha

Asalin hoton, @REALROCHAS/TWITTER


 

Tsohon Gwamnan Imo kuma ɗan Majalisar Dattawa, Sanata Rochas Okorocha, mai shekara 59, na daga cikin masu neman takarar shugaban ƙasa a APC.

Sai dai ana ƙila wa ƙala kan ko zai iya halartar tantancewar sakamakon yana tsare a hannun hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC bayan kamun da ta yi masa kwanakin baya.

Dimeji Bankole

Asalin hoton, Bankole/Facebok


 

Tsohon Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya, Honarabul Oladimeji Bankole na daga cikin waɗanda ake sa ran tantancewa a ranar Talata.

Bankole shi ne Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya na tara kuma shi ne kakakin majalisar mafi ƙarancin shekaru a tarihin Najeriya inda ya zama kakakin yana da shekara 37.

Sauran waɗanda ake sa ran tantancewa a ranar Talata

Gwamnan Cross River, Farfesa Ben Ayade

Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Dr. Ogbonnaya Onu

Tsohon Ministan Watsa Labarai, Chief Ikeobasi Mokelu

Tsohon Ministan Harkokin Neja Delta, Sanata Godswill Akpabio

Akwai kuma Mista Tein Jack-Rich

Saturday, February 12, 2022

GARAMBAWUL A ASO ROCK: Buhari ya naɗa Sani Zorro hadimin Uwargida Aisha, an sauya wa wasu hadimai wuraren aiki

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya naɗa fitaccen ɗan jarida, kuma tsohon ɗan majalisar tarayya daga Jigawa, Sani Zorro, hadimin uwargidan sa Aisha Buhari. Sani Zorro zai yi aiki a ofishin uwargidan shugaban kasa a matsayin babban maitaimaka mata kan harkokin hulɗa da jama’a da tsare-tsare. Bayan haka, a cikin sanarwar wanda Garba Shehu ya fidda ranar Asabar, shugaba Buhari ya amince da a sauya wa wasu manyan hadimai da ke aiki a ofishin uwargida Aisha wuraren aiki. An umarce su da su garzaya ofishin sakataren gwamnatin tarayya don sanin inda suka dosa. Waɗanda saiyin ya shafa sun haɗa da Mohammed Abdulrahman, babban likitan matar shugaban kasa, sai kuma Hadi Uba da Wole Aboderin. Sai dai kuma hadimar uwargida Aisha dake kula da harkokin yau da kullum da shirya bukukuwa, Zainab Kazeem ce kaɗai wanda garambawal ya wancakalar.

Wednesday, April 28, 2021

INEC ta tsayar da ranar zaɓen 2023 a Najeriya


Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya INEC ta tsayar da ranar zaɓen 2023 a ƙasar.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin taron yini ɗaya na sauraren dokar laifukan Zabe ta 2021, wanda kwamitin Majalisar Dattawa kan INEC ya shirya.

"Bisa dokar da aka kafa hukumar, zaɓen 2023 zai kasance ranar Asabar 18 ga watan Fabrairun 2023, wanda ya rage saura shekara ɗaya da wata Tara da mako biyu da kwana shida daga yau."

Shugaban Hukumar ya ce suna fatan tsara jadawalin zaɓen da zarar an kammala zaɓen gwamnan jihar Anambra wanda za a gudanar a ranar 6 ga Nuwamban 2021.

"Don yin yin hakan, ya kamata a samu tabbaci game da tsarin dokokin zaɓe don gudanar da zaɓen. Muna da yakinin cewa Majalisar Tarayya za ta yi abin da ya kamata cikin lokaci," in ji shugaban INEC.

Ya ce Hukumar ta matsu ta san tanadin doka da zai jagoranci gudanar da babban zaɓen na shekarar 2023.

Karin bayani na tafe..

Smart Adeyemi da Remi Tinubu: Matar Bola Tinubu ta soki Sanatan da ya ce babu tsaro a Najeriya

Wasu 'yan majalisar dattawan Najeriya sun yi musayar zafafan kalamai sakamakon rashin tsaron da ke ci gaba da ta'azzara a kasar.



Sanatocin, Smart Adeyemi daga jihar Kogi da Remi Tinubu daga jihar Lagos, suna cikin wadanda suka bayar da gudunmawa yayin muhawarar da majalisar dattawan kasar ta gudanar ranar Talata.

Majalisar ta yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari ya zage damtse domin magance rashin tsaron da kasar ke ci gaba da fama da ita tana mai shan alwashin ganawa da shi a kan batun.

A nata bangaren, majalisar wakilan kasar ta bukaci Shugaba Buhari ya ayyana dokar ta-baci a kan matsalar tsaro.


'Yan majalisun na yin kiran ne a yayin da ake ci gaba da kai hare-hare a kusan dukkan sassan kasar - daga rikicin masu garkuwa da mutane da 'yan fashin daji, zuwa hare-haren 'yan Boko Haram da na masu son ballewa daga kasar na kungiyar IPOB.

Sai dai kalaman da Sanata Smart Adeyemi ya yi cewa akwai bukatar daukar matakan gaggawa domin magance matsalar sun fusata takwararsa Sanata Remi Tinubu.

Dukkanin Sanatocin 'ya'yan jam'iyyar APC mai mulkin kasar ce.

Sanata Adeyemi ya ce: "Wannan ita ce matsalar tsaro mafi muni da muke fuskanta. A hakikanin gaskiya, wannan matsalar ta fi ta Yakin Basasa muni," in ji shi.

Ya kara da cewa "bai kamata mu rika siyasantar da wannan matsala ta tsaro ba. Babu wanda yake iya yin bacci da ido biyu a kasar nan — daga kudu zuwa arewa. Ba zan iya zuwa Kaduna ba inda aka haife ni saboda rashin tsaro."

A cewarsa, dole Shugaba Buhari ya nuna cewa shi ne shugaban kasar ta hanyar yin gaggawar magance wannan matsala.

Sai dai da alama wadannan kalamai ba su yi wa Sanata Remi Tinubu, matar jigon jam'iyyar APC Bola Tinubu, dadi ba.

Da take yin raddi a gare shi, ta ce Sanata Samart Adeyemi kura ne da fatar akuya.

Ta tambaye shi cewa: "Shin kai dan jam'iyyar PDP (Peoples Democratic Party) ne? Ko kai kura ce da fatar akuya?"

Ta ce a matsayinsa na dan jam'iyyar APC bai kamata ya rika irin wadannan kalamai ba.

Me 'yan Twitter suke cewa?

Wannan batu dai shi aka fi tattaunawa a kansa a shafin Twitter na Najeriya a ranar Laraba, inda 'Remi Tinubu' da 'Smart Adeyemi' suka kasance sunayen da ake amfani da su domin yin tsokaci kan batun.

Da yake tsokaci kan batun, FS Yusuf, ya bayyana cewa bai kamata a rika siyasantar da batun rashin tsaro ba, yana mai cewa "gaba-gadin da Remi Tinubu ta yi wajen gaya wa 'yan Najeirya cewa kasar ka iya konewa idan jam'iyyarsu maras alkibla za ta ci gaba da mulki, wani keta ne da rashin hankali."

Kauce wa Twitter, 1

Karshen labarin da aka sa a Twitter, 1

Ita kuwa Nefertiti ta yaba wa Sanata Smart Adeyemi wanda ta bayyana a matsayin wayayyen mutum wanda babu ruwansa da batun jam'iyya.


Thursday, December 17, 2020

Matsalolin Tsaro A kasar Mu.

Tsaro a kasarmu da namu laifi

Sau nawa muka aje ra'ayi, muka dukufa ga yiwa shugabaninmu da kasarmu addu'ar neman mafita da samun sauki akan wadanan masifun dake kara azzara da sanya al'umma cikin wahala da rashin kwanciyar hankali?

Sau nawa muka tausayawa masu rauni daga cikinmu ba tare da neman asani ba, ko muka sada zumunta ko muka ziyarci yan uwa ko makwabta dake fama da wahala don taimaka musu ko yin jaje ko tausayawa akan jarrabawar da aka aza musu?

Ko kayi gyara ayau, ko ka ci gaba da hangen laifin wasu kana take naka; don ganin kai ka hau wani tudun tsira, har da hura hanci abin kuma yana ta'azzara.

Wannan ba shine mafita ba, mafita itace, mu tuba, mu zauna mu yiwa kanmu karatun ta natsu don samun sauki da taimakon Ubangiji Allah (SWT).




Hakika wannan masifar ta wuce dora laifi akan shugabani su kadai, ko neman siyasantar da ita; ko ganin cewar, kai ka tsira, ba ruwanka da halin da wasu suke ciki. Tabbata kowa yana da rawar da zai taka ga samun nasara da ganin an shawo kan matsaloli da barazana da ake ciki akan tsaro, musifu da ake ta haduwa dasu a cikin al'umma.

Mu dukufa ga yiwa shugabani addu'a tagari da basu uzuri akan barazana da kalubalen da suke fuskanta ga gudanar da ayyukansu na lamuran mulki a yau; tare da sanya kasarmu da jihohinmu a cikin addu'oi ga neman sauki da maganin wannan lamarin baki daya.

Sha'anin tsaro fa ya wuce aikin gwamnati ko jami'an tsaro su kadai; kowanenmu mu sani, yana da hakki da dama mai yawa don bada gudumuwarsa ya taimakawa da shawara, addu'a don samun nasara akan yaki da wadanan masifun a gida, unguwa, gari, karamar hukuma, da jaha ko kasa baki daya.

Mu yiwa juna uzuri da fatan alheri da taimakawa ga bayar da rahoto ko bayanai akan dukkan wani ko wasu dake da barazana ga zaman lafiya al'umma.

Mu daina jiran sai ta faru, muce ai daman, mun san haka zata kasance. My sani dukkanmu makiyaya ne, ba shakka sai Allah Ya tambaye mu daya bayan daya akan abin da aka bamu kiwo da yadda muka aiwatar dashi.

Allah Yayi ma al'ummarmu mafita ya tallafawa shugabaninmu dake akan gaskiya ga wannan aikin na yaki da ta'addanci da sauran masifu dake addabar jama'a. Amin.

- Yusuf Dingyadi, Sokoto

ZABEN 2023: Jonathan Na Da Damar Tsayawa Takarar Shugabancin Nijeriya A Zabe Na Gaba, Cewar Jam'iyyar PDP

ZABEN 2023: Jonathan Na Da Damar Tsayawa Takarar Shugabancin Nijeriya A Zabe Na Gaba, Cewar Jam'iyyar PDP

Daga Comr Abba Sani Pantami

Jam'iyyar PDP da ta mulki Najeriya na tsawon shekaru 16 ta ce tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan na da hurumin tsayawa takarar zaben shekarar 2023 idan yana bukata.

Shugaban Jam’iyyar Uche Secondus ya sanar da haka, inda yace cewa ya zuwa yanzu Jam’iyyar ba ta yanke hukunci dangane da karba karba ko inda ake sa ran ‘dan takaran zaben shekarer 2023 zai fito ba.

Secondus ya ce Jam’iyyar na jiran rahotan kwamitin da ke nazari kan abın da ya faru lokacin zaben shekarar 2019 daga hannun kwamitin da Gwamnan Bauchi Bala Muhammed ke jagoranci, domin gano abin da ya sa Jam’iyyar ta sha kaye.

Bayan kwashe shekaru 6 a karagar mulki, Jonathan ya fadi zaben shekarar 2015, lokacin da Jam’iyyar APC ta gabatar da Muhammadu Buhari a matsayin ‘dan takara, yayın da tsohon shugaba Jonathan yaki tsayawa zaben shekarar 2019.

Shugaban PDP ya gargadi Jam’iyyar APC mai mulki da ta daina kusantar ‘yayan ta ganin yadda ta dauke Gwamnan Ebonyi, David Umahi, yayin da kuma take zawarcin shugaba Goodluck Jonathan.


Sunday, December 13, 2020

Ɗaliban Kankara: Har yanzu ba a ji ɗuriyar 'ɗalibai 333' ba

Ɗaliban Kankara: Har yanzu ba a ji ɗuriyar 'ɗalibai 333' ba


Har yanzu ba a ji ɗuriyar ɗaliban makarantar sakandaren Kankara ta jihar Katsinan Najeriya da ƴan bindiga suka yi awon gaba da su ranar Juma'a ba.

Hakan na faruwa ne duk da zaratan sojoji da 'yan sanda da gwamnatin Najeriya ta aika domin gano ɗaliban.

Mai magana da yawun shugaban ƙasar Malam Garba Shehu ya ce an aika zaratan sojojin ƙasa da na sama domin nemo ɗaliban baya ga jami'an 'yan sanda na musamman da Babban Sifeton 'yan sandan ƙasar Mohammed Adamu ya bayar da uarnin aikawa.

Hasalima Babban hafsan sojan ƙasa na Najeriya Janar Tukur Buratai ya isa garin Kankara ranar Lahadi.

Bayanai sun ce Janar Buratai ya gana da rundunar soji da ta ƙaddamar da binciken gano ɗaliban.

Babban Hafsan sojan na Najeriya ya tafi Kankara ne tare da tawagar gwamnatin Tarayya da ta ƙunshi ministan tsaro Janar Salihi Magashi mai ritaya da kuma mai ba shugaban ƙasa shawara kan sha'anin tsaro.

Bayanai masu cin karo da juna

Gwamnatin Katsina ta tabbatar da cewa ɗalibai 333 ne suka ɓata bayan harin da ƴan bindiga suka kai makarantar sakandaren ta Kankara.

Wata majiyar gwamnatin Katsina ta shaida wa BBC cewa Gwamna Masari ya tabbatar da hakan ne ga tawagar gwamnatin Tarayya ƙarkashin jagorancin bai bai wa shugaban ƙasa shawara kan sha'anin tsaro Babagana Monguno.

Gwamnan ya ce ana ci gaba da bincike a daji domin gano ɗaliban da ake tunanin ƴan bindiga sun sace.

Sai dai Malam Garba Shehu ya shaida wa BBC cewa yara da dama sun gudo yana mai cewa yara 10 ne kawai suka rage hannun ƴan bindigar.

A cewarsa, yaran da suka tsere daga hannun maharan sun ce yara 10 ne ke hannun ɓarayin ƙasa da yawan ɗaliban da malaman makarantar suka bayyana.

"Wasu daga cikin yaran da suka gudu daga daji sun ce yara 10 ne ƴan bindigar suke garkuwa da su," in ji shi.

Sai dai ya ce sai an bincika sannan domin sun warwatsu a daji saboda ɗimauta daga ƙarar harbe-harben bindiga.

Kakakin na shugaban Najeriya ya ƙara da cewa jami'an tsaro sun yi wa yankin da suke tunanin ƴan bindiga na garkuwa da ɗaliban da suka sace a Kankara ƙawanya.

Ya kuma ce kusan ɗalibai 200 suka dawo gida kuma wasu daga cikin iyayen yaran sun karɓi ƴaƴansu da suka fito daga daji yayin da kuma ake ƙoƙarin tantance yawansu da waɗanda suka dawo.

Mata sun yi zanga-zanga


Wasu hotuna da aka yaɗa a shafukan zumunta sun nuna wata mace na jagorantar zanga-zanga a garin Katsina domin matsa wa gwamnati lamba kan ceto yaran nasu.

Matan riƙe da kwalaye sun buƙaci gwamnatin Najeriya ta yi gaggawar ceto ɗaliban suna masu yin tur da sace su.

A daren Juma'a ne ƴan bindiga suka afka makarantar sakandaren ta maza zalla da ke garin Ƙanƙara suka sace ɗaliban.

Wasu bayanai sun ce akwai ɗalibai fiye da 600 a yayin da aka kai harin, sai dai kakakin rundunar 'yan sandan Katsina, DSP Gambo Isa, ya shaida wa BBC cewa tuni aka gano ɗalibai fiye da 200.

Iyayen ɗaliban makarantar na jiran tsammani game da labarin ƴaƴansu, inda suka je makarantar domin sanin halin da 'ya'yansu ke ciki.

Me hukumomi suka ce da farko?



Sanarwar da Malam Garba Shehu ya fitar ranar Asabar ta ce an gano maɓoyar maharan har ma sun yi artabu da jami'an tsaro.

Rundunar ƴan sanda ta ce an kashe ɗaya daga cikin maharan kuma jami'inta ɗaya ya ji rauni, yayin da ta ce sufeton janar na ƴan sandan Najeriya ya tura ƙarin jami'ai domin kuɓutar da ɗaliban.

Ƴan Najeriya da iyayen ɗaliban na dakon sanarwa daga gwamnatin tarayya ko ta jihar Katsina game da inda aka kwana kan batun kuɓutar da ɗaliban na makarantar Kankara.

Shugaba Buhari ya yi Allah-wadai da sace ɗaliban amma gwamnatinsa na fuskantar matsin lamba, musamman kan yadda lamarin tsaro ke ƙara taɓarɓarewa a arewacin Najeriya.

Sace ɗaliban na zuwa bayan a ƙarshen watan da ta ya gabata, ƴan Boko Haram suka yi wa manoma yankan rago a jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashi.

Iƴayen yaran na cikin ɗimauta



Iyayen yaran da aka sace sun bayyana wa BBC irin mawuyacin halin da suka shiga tun da aka sace 'ya'yansu.

Mahaifin wasu ɗalibai biyu ya shaida mana cewa tun da lamarin ya faru suke cikin damuwa "domin duk lokacin da aka ce yaronka ya ɓata dole ka shiga damuwa, don gara ma a ce mutuwa ya yi."

Ya ce mahaifiyar yaran ta shiga damuwa sosai ko da yake sun fawwala komai ga Allah.

Gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari, wanda ya ziyarci makarantar ranar Asabar, ya bayar da umarnin rufe ɗaukacin makarantun sakandare na kwana da ke faɗin jihar.

Wasiƙa daga Afrika: Me ya sa ake barazana ga 'yan jarida a Najeriya?

Wasiƙa daga Afrika: Me ya sa ake barazana ga 'yan jarida a Najeriya?


Tsohon minista Femi Fani-Kayode ya yi ta cin mutuncin ɗan jaridar kamar wanda aka yi wa baki

Cikin jerin wasiƙun da muke samu daga 'ƴan jarida daga Afirka, tsohon babban editan jaridar Daily Trust, Mannir Dan Ali ya duba ƙalubalen da 'ƴan jarida ke fuskanta a yayin gudanar da ayyukansu.

A Najeriya har yanzu ana tambayar ko me ya sa jami'an gwamnati suke yi wa 'ƴan jarida kallon yaransu.

Wannan ya biyo bayan ƙurar da ta tashi sakamakon cin mutuncin da tsohon minista a Najeriya, Femi Fani Kayode kuma ɗan jam'iyyar adawa ta PDP ya yi wa wani ɗan jarida.

Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta ya nuna yadda Femi Fani-Kayode ya fusata saboda wata tambayar da ɗan jarida, Eyo Charles ya yi masa yayin wata hira da 'yan jarida.

Eyo

Mr Fani-Kayode, wanda ba ya riƙe da wani muƙami a gwamnati ko Jam'iyyar PDP, ya fito bainar jama'a yana rangadin ayyukan gwamnoni a sassan jihohin Najeriya.

Duk rangadin da ya gudanar, yana kiran taron ƴan jarida domin yaba wa ayyukan.

A Calabar ne babban birnin Cross River, jiha ta uku da ya kai ziyara a watannin da suka gabata inda Mista Fani-Kayode ya nuna bacin ransa lokacin da Charles ya tambaye shi kan wanda ke ɗaukar nauyin rangadin da yake: "Ba ka faɗa muna wanda ke ɗaukar nauyin tafiye-tafiyen da kake ba..."

Maimakon ma ya bari ɗan jaridar ya idar da tambayarsa, kawia Fani-Kayode ya kira shi "wawa" tare da cewa ya yi kama da talaka da ke karɓar cin hanci, kamar yadda ake zargin ƴan jarida na karɓar na goro da ake kira "brown envelopes" a Ingilishi.

Ni mun taɓa samun saɓani da shi, lokacin da yake cikin majalisar ministoci tsohon shugaba Olusegun Obasanjo shekaru goma da suka gabata.

Ya wuce zagi, ya faru ne a fadar shugaban ƙasa da ake kira Aso Rock inda ya yi barazanar zai mare ni, sai da sauran ƴan jarida suka shiga tsakani.

Ban san dalilin da ya sa a lokacin ya fusata ba; sai daga baya na gano cewa ashe saboda wata hirar da ya yi da BBC game da kudirin Obasanjo na tazarce.

Hirar ta ja hankali kuma shi ne dalilin da ya sa ya nemi ya huce akaina a matsayin wakilin BBC a fadar shugaban ƙasa a lokacin.

Ba wai Mista Fani-Kayode ba ne kaɗai ke ɗaukar ƴan jarida a matsayin abin haushi ba.

A watannin baya, gwamnan jihar Ebonyi a kudu maso gabashin Najeriya ya kori wasu ƴan jarida guda biyu a yankin kan abin da ya kira yadda suke bayar da rahotannin da ba su dace ba game da jihar.

"Idan kana tunanin kana da alƙalami, mu muna da bulala," kamar yadda gwamnan ya yi barazana ta hanyar amfani da wata kalmar salon magana ta linzamin doki.

Caccakar gwamna da sukar matakin a kafofin yaɗa labarai ya tilasta masa janye haramcin.

2px presentational grey line

Shekaru da dama a jaridar Daily Trust, dole muka janye wakili daga jiha bayan wasu zauna gari banza sun masa duka a wani taro bayan gwamna ya nuna ba so n rahotanninsa.

A cikin martaninta kan abin da ya faru kwanaki game da Fani-Kayode, Amnesty International ta yi allawadai da yadda aka walaƙanta ɗan jaridar.

"Haƙƙin ƴan jarida ne su tabbatar da gaskiya domin mutane kuma bai dace a yi masu barazana ba ko zaginsu don sun yi tambaya ba," a cewar sanarwar ƙungiyar ta kare haƙƙin bil'adama.

Dan Ali

Suka daga bangarori da dama, ya tilastawa Mista Fani-Kayode neman afuwa ga ɗan jaridar - ko da yake har yanzu yana yi wa Daily Trust barazanar cewa zai ɗauki matakin shari'a kan wani zane da jaridar ta yi game da batun.

A bayyane yake wannan ba shi ne na ƙarshe ba kan takun-saƙa tsakanin ƴan jarida da kuma manyan masu faɗa aji a Najeriya.

Wasu hukumomin gwamnati da manyan kamfanoni suna haramta ba kafafen yaɗa labarai tallace-tallace saboda ba su jin daɗin rahotannin da suke bayar wa.

Baya ga barazana da kuma furta munanan kalamai, akwai kuma wasu hanyoyi da kafofin yada labarai a Najeriya a ƙasashen Afirka suke tafiya a haka.

Saboda akwai ƙarancin albashi wani lokaci ma ba a biyan albashin a wasu kafafen yaɗa labarai, wanda hakan ke nufin wasu ƴan jaridar sun dogara ne da wanda zai biya su.

Wasu ma sukan buƙaci sai an biya su kuɗi kafin su ɗauki labari.

Fadar mabarata

Bisa ƙwarewa ta a matsayin ɗan jarida a Najeriya, ba wai masu hannu da shuni ba ko manyan masu faɗa aji ne suka ɗauki ƴan jarida a matsayin masu karbar na goro ba.

Wani babban misali shi ne wani shugaban mabarata a matattarar da ake zube shara a Ijora Badia a Legas.

Na tafi don na yi hira da shi a BBC a wajajen 1990 domin gano abin da ya yi kan yunƙurin hukumomi na janye mabarata daga saman titi zuwa wata cibiyar farfaɗo da su.

Yana wajen da ya kira fadarsa da aka gina can saman katakayyan shara.

Bayan haka, ya dage wai sai na karɓi kuɗi daga hannunsa.


Wasu 'yan jarida suna son a rika ba su kudi idan suka halarci taro

Na ƙi karɓa har sai da na yi masa dogon bayani don ya fahimci cewa ba ni buƙatar na karɓi kudi daga wajensa don na gudanar da aiki na.

A kwana baya a ofishin jekadancin Amurka ranar bikin ƴancin faɗin albarkacin baki, wani ƙaramin dan jarida yake son sanin dalilin da ya sa babu kyau a karɓi kuɗi a yayin ɗaukar rahoto a wajen wani taro.

Yana ganin kamar biyan waɗanda suka yi jawabi ne a wurin taron.

Ɗaya daga cikin masu jawabi a wurin taron ya yi masa bayani ta hanyar amfani da karin magana cewa "hannun bai bayarwa a kullum yana saman hannun mai karɓa" - wato yana nufin idan ɗan jarida yana karɓar irin waɗannan kyaututtukan, to shi ko ita yana da wahala su iya yin adalci ko kuma yin tambaya mai tsauri.

Abin baƙin ciki a Najeriya a irin wannan yanayin da ba a irin waɗannan tambayoyin, ɗan jarida na iya samun kansa a irin abin da Fani-Kayode ya aikata.